19 Afirilu 2021 - 14:42
Matsalar Tsaro Na Ci Gaba Da Addabar Wasu Yankunan Nijar

Yankunan da suke fuskanci kai hare-hare a kwanakin farko na watan azumin Ramadan mai alfarma sun kunshi Maine Soroa da ke gundumar Diffa, da kuma Gairorou a gundumar Tillaberi.

ABNA24 : An kai hare-haren ne dai a ranakun Alhamis da kuma Asabar, da su ka yi sanadin mutuwar mutane da dama.

Yankin Tilliberi da ke Arewa maso yamma kuma kusa da iyaka da kasar Mali yana daya daga cikin inda masu dauke da makamai su ka tsananta kai hare-hare a cikin Nijar. Sai kuma yankin Diffa dake Kudu maso gabashin kasar a gabar tafkin Chadi da kungiyar Bokoharam take kai nata hare-haren.

342/